in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara kada kuri'u a zagaye na Biyu na babban zaben kasar Mali
2013-08-11 16:53:52 cri
Rahotanni da kasar Mali na bayyana cewa dubun dubatar al'ummar kasar ne suka fara kada kuri'unsu da misalin karfe 8 na safiyar Lahadin nan. A zagayen babban zaben kasar na biyu da ake fatan zai zamo raba gardama tsakanin tsohon firaministan kasar Ibrahim Boubacar Keita, da tsohon ministan harkokin wajen kasar Soumaila Cisse, wadanda suka zamo a sahun gaba, yayin zagaye na farko na zaben da ya gabata.

Har ila yau rahotanni sun tabbatar da cewa za a rufe runfunan zaben ne da misalin karfe 6 na yammaci, a kuma sanar da sakamakon zaben nan da kwanaki 5 masu zuwa. Kimanin 'yan kasar ta Mali miliyan 6.8 ne ake sa ran za su sake kada kuri'unsu a wannan zagaye.

A wani labarin mai alaka da wannan kuma, jagoran tawagar jami'an sa ido ga zaben kasar ta Mali na kungiyar AU Edem Kodjo, ya yi kira ga daukacin al'ummar kasar ta Mali da su fito kwansu-da-kwarkwata, domin kada kuri'unsu, Kodjo wanda ya yi wannan kira ranar Asabar 9 ga wata, ya ce zagayen zaben na farko ya gudana ba tare da wani korafin aikata magudi ba, don haka ya zama wajibi ga al'ummar kasar su baiwa zagayen na biyu cikakken muhimmanci da ya dace. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China