in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
EU ta kara tura masu sa ido ga kasar Mali don sa ido ga jefa kuri'u a zaben shugaban kasar zagaye na biyu
2013-08-10 16:11:44 cri
A ranar 9 ga wata a Bamako, babban birnin kasar Mali, mataimakiyar shugaban tawagar masu sa ido a zaben shugaban kasar Mali ta kungiyar EU Espinoza Maria del Rosario ta bayyana cewa, kungiyar EU za ta kara tura masu sa ido 27 ga kasar Mali don sa ido ga jefa kuri'u a zaben shugaban kasar zagaye na biyu.

Madam Espinoza ta ce, ya zuwa yanzu kungiyar EU ta tura masu sa ido fiye da 100 ga kasar Mali, wadandan za su sa ido kan dukkan ayyukan zaben shugaban kasar da odar yin zaben a manyan yankuna 5 na kasar kamar Segou, Kayes, Mopti da dai sauransu.

Kafin wannan, hukumar zaben kasar Mali mai zaman kanta ta bayyana cewa, tawagar masu sa ido dake kunshe da membobi fiye da dubu 5 daga kasar da sauran kasashen duniya ta dauki nauyin sa ido ga zaben shugaban kasar. Yawancin masu sa ido daga kasar Mali sun zo ne daga wasu kungiyoyi da hukumomi masu zaman kansu a kasar. Kana yawancin masu sa ido na kasa da kasa sun zo daga kungiyar AU, EU, kawancen kasashe masu amfani da harshen Faransanci, ECOWAS da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China