in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun sojin a Najeriya sun kaddamar da simame a jihar Sakkwato
2013-08-11 16:31:33 cri
Rahotanni daga Najeriya na bayyana cewa rundunar sojin kasar ta kaddamar da wani simame na musamman a jihar Sakkwato, da nufin kakkabe 'ya'yan kungiyar nan ta Boko Haram, wadanda ake zargin na tserewa don samun mafaka a jihar, sakamakon kafa dokar ta baci a manyan sassanoninsu dake jihohin Borno, da Adamawa da kuma jihar Yobe.

Da yake tabbatar da aukuwar hakan, kakakin rundunar dake jihar ta Sakkwato, Yahaya Musa ya ce, an kai simame maboyar 'ya'yan kungiyar ta Boko Haram dake unguwar Gidan-Igwai a ranar Asabar 10 ga wata, bayan samun wasu bayanan sirri. Musa ya ce dukkanin matakan da ake dauka na da nasaba da burin rundunar, na tabbatar da doka da oda, tare da kare rayukan al'umma daga barazanar ayyukan 'yan ta da kayar baya.

Daga nan sai ya tabbatar da aniyar jami'an tsaro, ta tabbatar da gurfanar da dukkanin wadanda aka kama sakamakon wannan farmaki gaban kuliya, kamar yadda doka ta tanada.

Wannan dai mataki na zuwa ne dai dai lokacin da ake ci gaba da fargaba, don gane da yiwuwar cimma nasarar shirin gwamnatin tarayyar Najeriyar na yi wa 'ya'yan kungiyar ta Boko Haram afuwa, wanda aka fara cikin watan Afrilun da ya gabata. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China