in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojin Najeriya ta dora laifin asarar man fetur kan kamfanonin mai
2013-07-31 10:09:40 cri

A ranar Talata 30 ga wata, sojin Najeriya ta dorawa kamfanonin mai na Shell da Agip laifin asarar man fetur da yawansa ya kai ganga 190,000 kowace rana a filayen hako mai dake jihar Bayelsa a kudancin kasar.

Wannan asara ya sa an samu raguwar kudin shiga a jihar inda yayi kasa daga naira biliyan 12.4 a watan Mayu zuwa naira biliyan 9 a watan Yuni, bisa kididdiga ta wata wata da gwamnan jihar Seriake Dickson ya bayar.

Kamfanonin man guda biyu sun nuna kasawarsu a wajen samar da mai a nau'rorinsu dake jihar Bayelsa domin su wanke kansu daga dukkan wani nauyi a bangaren masu sayen danyen mai. Sun kuma bayyana cewa an samu wannan koma baya ne saboda yadda ake satar mai a jihar.

A nasa bangare, mai magana da yawun hukumar tsaro ta hadin gwiwa a yankin Niger Delta (JTF), Onyema Nwachukwu yace da kamfanonin sun bi shawarar rahotanni da hukumar ta ba su, da hakan bai auku ba.(Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China