in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu fashewar boma-bomai a kasar Iraki
2013-03-20 14:40:52 cri

A ranar 19 ga wata, an samu fashewar boma-bomai sau da dama a birnin Baghdad da kewayensa, wadanda suka haddasa mutuwar mutane kimanin 60, kana mutane fiye da 200 suka ji rauni.

Jim kadan bayan abkuwar lamarin, ofishin kakakin babban sakataren MDD ya bayar da wata sanarwa, inda ya ce, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi Allah wadai da fashewar boma-boman a Baghdad, babban birnin kasar Iraki, tare da nuna jajantawa ga iyalan mutanen da suka mutu a sakamakon lamarin. Wakilin musamman na babban sakataren MDD mai kula da batun kasar Iraki Martin Kobler shi ma ya bayar da wata sanarwa a wannan rana, inda ya yi tir da wannan lamari, kana ya ce, babu wasu dalilan aikata wadannan hare-hare ba.

Ranar 20 ga watan Maris rana za ta cika shekaru 10 da barkewar yakin kasar Iraki. A kwanakin baya, an sha samun hare-hare da tashe-tashen hankali dake da nasaba da addini a kasar Iraki, lamarin dake kara ingiza kasar cikin rashin zaman lafiya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China