in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ba da lambar yabo ga sojojin kiyaye zaman lafiya na kasar Sin
2013-08-09 20:29:04 cri
MDD ta ba da lambar yabon kiyaye zaman lafiya ga duk sojojin Sin 218, wadannan sojoji dai 218 sun zo daga rundunar sojan dake yankin Lanzhou, wadanda suka hada da sojojin injiniyoyi 175 da sojojin ba da jiyya 43.

Ita dai rundunar sojan kiyaye zaman lafiya ta kasar Sin zagaye na 15 ta kammala aikinta na tsawon watanni 8, kuma yanzu haka, sojojin Sin 118 daga cikinsu sun riga sun sauka a filin jirgin saman Xianyang dake birnin Xi'an na kasar Sin a ranar Jumma'a 9 ga wata.

Wannan rundunar soja ta tashi zuwa yankin Bukavu na kasar Kongo Kinshasa a watan Nuwamba na bara domin gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya, a lokacin kuma, gaba daya hafsoshi da sojojin sun gudanar da aikin yadda ya kamata, tare da samun amincewar tawagar musamman ta MDD kan tabbatar da zaman lafiya a Kongo Kinshasa, da rundunonin sojan kiyaye zaman lafiya na kasa da kasa, da kuma gwamnati da jama'ar wurin. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China