in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaro ta MDD ta kara yawn lokacin aikin kafa zaman lafiya a Guine-Bisau
2013-02-23 16:40:29 cri
A ranar Jumma'a 22 ga wata ne kwamitin tsaro na MDD ya zartas da kudurin kara yawan lokacin aikin ofishin kafa zaman lafiya a kasar Guinea-Bisau da ake kira UNIOGBIS zuwa ranar 31 ga watan Maris na shekarar 2013.

Kwamitin mai mambobi 15 ya kuma yi kira ga masu ruwa da tsaki kan wannan kuduri da su ci gaba da kokarin inganta tattaunawa ta siyasa a cikin kasar don a samu cimma kafa yanayin da ya dace na gudanar da zabe cikin adalci wanda kuma zai samu karbuwa ga dukkan jama'ar kasar domin a samu dawo da oda ta tsarin mulkin kasa gami da dorewa na tsawon lokaci a kasar.

Kwamitin ya yi nunin cewa ya damu matuka dangane da yanayi da ake ciki a kasar bayan juyin mulki na soji da aka yi a kasar a watan Aprilun shekarar da ta wuce wadda ya yi sanadin hargitsa shirin zabe aka tashi babu sakamako.

Ayyuka da aka damkawa ofishin kafa zaman lafiya a kasar Guinea-Bisau na MDD sun kunshi kawo inganci a cibiyoyi, kiyaye doka, ba da hadin kai ga shirin kawo sulhu da kuma taimakawa hukumomi a yaki da fataucin miyagun kwayoyi.

Kudurin na mai bayyana cewa babban sakataren MDD Ban Ki Moon zai ba da rahoto kan kasar Guinea-Bisau a ranar 30 ga watan Aprilun shekarar 2013 domin a tantance irin karin gudummawa da kasar ke bukata. (Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China