in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan tsaron kasar Mali bai yi fatali da girke sojojin MDD a kasarsa ba
2013-02-12 16:58:18 cri
A wani taron manema labaru da ya gudana a Bamako a Litinin 11 ga wata, Yamoussa Camara, ministan tsaron kasar Mali, ya ce bai ga wata matsala game da girke sojojin MDD a kasarsaba.

A cewar minista Camara, da ma ba a taba shirin girke sojojin wanzar da zaman lafiya na MDD a kasar ba, domin ba a san karfin da masu tsattsauran ra'ayin addini suke da shi ba. Wannan dalili ne ya sanya aka yi taruruka da yawa kafin a tura sojojin kasa da kasa masu tallafawa kasar Mali na MISMA.

Sai dai ya ce a ganinsa, duk da cewa kasashen kungiyar ECOWAS sun tura sojoji zuwa kasar Mali, amma ba za a samu damar cimma buri ba cikin sauri in ba tare da tallafi daga wata kasa mai karfi kamar Faransa ba.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China