in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta taya shugaban kasar Zimbabwe murna bisa nasarar da ya samu a babban zaben
2013-08-08 20:22:29 cri
A ranar Alhamis 8 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin, Hong Lei ya bayyana cewa, Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya buga masa waya ga takwaransa na kasar Zimbabwe Robert Mugabe domin taya shi murna bisa nasarar da ya samu da shi da Jam'iyarsa ta ZANU-PF na lashe babban zaben kasar.

Game da wani ra'ayin kasar Sin ganin yanzu an riga an gabatar da sakamakon babban zaben, inda shugaba Mugabe ya yi nasara, Mr Hong Lei ya ce bisa sakamakon da kwamitin zaben kasar Zimbabwe ya gabatar a kwanan baya, ya nuna cewa shugaba Mugabe da jam'iyyar ZANU-PF dake karkashin jagorancinsa sun lashe babban zaben. Don haka Sin take taya kasar murna game da hakan.

Ban da haka, Hong ya yi bayanin cewa, a matsayin aminiyar Zimbabwe, Sin tana fatan Zimbabwe za ta kara samun ci gaba bisa wannan babban zabe, kuma Sin za ta ba da goyon baya ga kokarin Zimbabwe na tabbatar da zaman lafiya da neman samun ci gaba.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China