in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manyan jami'an gwamnatin Amurka sun gana kan batun barazanar harin ta'addanci
2013-08-04 16:38:46 cri
A ranar Asabar 3 ga watan ne manyan jami'an gwamnatin kasar Amurka suka yi wata ganawa ta musamman a fadar White House, domin tattauna batutuwan da suka shafi barazanar kaiwa cibiyoyin kasar dake yankin Gabas ta Tsakiya hare-hare.

Wannan dai taro na masu ruwa da tsaki ya biyo bayan rufe wasu daga cikin ofisoshin diplomasiyyar kasar ta Amurka da aka ayyana gudanarwa a ranar Lahadin nan.

Wata sanarwar da fadar ta White House ta fitar ta bayyana cewa, babbar mai ba da shawara ta fuskar tsaro Susan Rice ce ta jagoranci taron, wanda ya samu halartar manyan mataimaka ga shugaba Barack Obama, da manyan sakatarori, da kuma shuwagabannin hukumomin tsaron cikin gida da waje. Sanarwar ta ce, makasudin taron na ranar Asabar shi ne sake nazartar matakan da aka rigaya aka dauka, tare da tattauna matakan da suka dace a dauka a nan gaba.

A cewar waccan sanarwa, duba da muhimmancin da wannan batu ke da shi, babbar mataimakiya ga shugaban kasa kan harkokin tsaro, da yaki da ta'addanci Lisa Monaco ta gana da sassan hukumomin tsaro daban daban cikin satin da ya gabata, kuma tuni aka yi wa shugaba Obama cikakken bayanin halin da ake ciki.

A wani ci gaban kuma a yau Lahadi ne kasashen Birtaniya da Faransa da Jamus suka bayyana aniyarsu ta rufe nasu ofisoshin diplomasiyya dake kasar Yemen tsawon a kalla makwanni biyu, yayin da ita ma kasar Canada ta bayyana rufe ofishinta dake kasar Bangaladesh. Ana dai ganin daukar wannan mataki na da nasaba da ayyana rufe ofisoshin diplomasiyyar Amurka da aka yi a kasashen musulmi daban daban, sakamakon bayanan sirrin da hukumomin tsaron kasar suka ce sun bankado. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China