in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fata jam'iyyun Zimbabwe za su amince da sakamakon zabe
2013-08-03 20:58:48 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkoin wajen Sin Hua Chunying ta baiyana yau Asabar cewa, Sin na fata Jam'iyyun siyasar kasar Zimbabwe za su amince da sakamakon zaben da aka yi.

Hua ta fadi hakan ne yayin da take amsa tambaya dangane da matsayar Sin game da babban zaben kasar Zimbabwe da aka yi ranar Laraba.

Ta ce gwamnatin kasar Sin ta tura tawagar masu sa ido karkashin jagorancin tsohon jakadan Sin kan harkokin Afirka, Liu Guijin.

Tawagar ta baiyana cewa an yi zaben cikin lumana, natsuwa da kuma inganci kana an jefa kuri'a ba tare da tangarda ba cikin zamma.

Kasar Sin na taya kasar Zimbabwe murna dangane da nasarar gudanar da zaben, ta kuma kara da cewa Sin na mai nuna gamsuwa kan zammar 'yan kasar Zimbabwe game da kishin kasa da 'yanci.

Mai magana da yawun gwamnatin ta Sin ta yi kira ga al'ummar kasa da kasa su mutunta zabin mutanen kasar Zimbabwe.

Ta ce tana fata 'yan kasar Zimbabwe za su kuduri fara wani sabon shafin rayuwa a kasarsu cikin zaman lafiya, sulhu, bunkasa da kuma farfadowar kasar. (Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China