in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar Liberia ta yaddda inganta yin hadin gwiwa da kasar Sin
2013-08-03 17:04:42 cri
Ranar 1 ga wata, a birnin Monrovia, hedkwatar kasar Liberia, yayin da shugaba Ellen Johnson-Sirleaf ta kasar take zantawa da manema labaru, ta bayyana cewa, kasarta tana daraja dankon zumuncin da ke tsakaninta da kasar Sin. Kuma nan gaba za ta kara inganta yin hadin gwiwar abokantaka a tsakanin kasashen 2 domin bunkasuwar dangantakar da ke tsakaninsu za ta kawo musu duka alheri.

Madam Johnson-Sirleaf ta kara da cewa, kasarta ta Liberia da kasar Sin sun yi hadin gwiwa a fannoni daban daban. Masana'antun kasar Sin suna zuba jari a harkokin raya albarkatun ma'adinai a Liberia, kana suna gina hanyoyin mota a kasar, inda lamarin ya samar da kyakkyawan sakamako.

Har wa yau shugabar ta ce, kasarta ta gode wa kasar Sin sosai bisa goyon bayan da take nuna mata. Yanzu kasashen 2 suna kara raya huldar da ke tsakaninsu yadda ya kamata.

Ban da haka, madam Johnson-Sirleaf ta jaddada cewa, a kokarin samar da kyakkyawan yanayi a fuskar raya tattalin arziki da zuba jari, gwamnatin Liberia tana kokarin kyautata tsarin dokokinta, da kuma kara bunkasa ayyukan amfanin jama'a, kamar hanyoyin mota, samar da wutar lantarki da dai sauransu. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China