in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar zabe ta kasar Liberia ta fitar da sakamakon karshe
2011-10-26 14:57:02 cri
A ranar 25 ga wata kamfanin dillancin labaru ta kasar Sin Xinhua ta bada labarin cewa hukumar zabe ta kasar Liberia ta fitar da sakamakon karshe na zaben shugaban kasa da 'yan majalisun dokokin da aka yi ranar 11 ga wannan watan,tana mai cewa cikin 'yan takara 16 na neman kujerar shugaban kasa babu wanda ya samu cikakken rinjaye da zai bashi dammar lashe zaben.

Dokar zaben kasar Liberia ta ce dole ne dan takarar shugaban kasa ya samu kashi 50 cikin 100 kana kuma da kuri'a guda daya cikin wanda aka kirga kamar yadda sharadi na 83b na kundin mulkin kasar na 1986 ya gindaya.

A taron manema labaru yammacin talatan nan,shugaban hukumar zaben James Fromayan yace ba'a cika sharuddan ba lokacin zaben da ya gabata don haka za'a yi zaben raba gardama a ranar 8 ga watan gobe wato nuwamba.

A ta bakin Mr Fromayan,za'a gudanar da zaben raba gardama tsakanin 'yan takara biyu da suka fi samun kuri'u wandanda suka hada da Ellen Johnson-Sirleaf na jam'iyyar Unity Party da kuma Winston Tubman na jam'iyyar Congress of Democratic Change.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China