in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta jaddada kin amincewarta da dakatar da ita da AU tayi
2013-07-31 10:34:25 cri
Mahukuntar kasar Masar a ranar Talatar nan ta sake jaddada kin amincewarta da kungiyar Tarayyar kasashen Afrika AU ta yi masu na dakatar da kasar daga duk wani harkokinta.

Wannan kin amincewa an sake nanata shi ne lokacin da Alpha Omar Konare, Jagorar mutane 9 na kungiyar AU din da a yanzu haka suke ziyara a kasar ta Masar, wanda ya yi bayanin bayanin cewa wannan shawara ba ta da wani nufi akan matsayin kasar a nahiyar Afrika.

Kwanaki biyu bayan hambarar da Shugaba Mohammed Morsy na Jam'iyar 'yan uwa musulmi a ranar 3 ga watan Yulin nan, kwamitin wanzar da zaman lafiya da tsaro na kungiyar AU ta sanar da dakatar da kasar daga duk wani harkokinta, tana mai bayyana hambarar da gwamnatin Morsy a matsayin wani aikin da ba ya cikin ka'ida.

A nata bangaren kasar Masar ta tura babbar tawagarta zuwa ga wassu kasashen nahiyar domin bayyana ra'ayinta game da wannan mataki, tana mai bukatar kungiyar da ta sake shawararta.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China