in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar jami'ar kungiyar EU ta sake zuwa kasar Masar domin shiga-tsakani kan rikicin kasar
2013-07-30 15:12:50 cri
A ranar 29 ga wata, fadar shugaban kasar Masar ta ba da sanarwa cewa, a wannan rana, mataimakin shugaban gwamnatin wucin gadi mai kula da dangantakar kasa da kasa na kasar Masar Mohamed M.El Baradei ya yi shawarwari da Catherine Ashton wakiliyar kungiyar EU da ke kula da harkokin diplomasiyya da batun tsaro, inda suka tattauna yadda za a kawo karshen rikicin siyasa a kasar.

Yayin da Baradei ke ganawa da Ashton, ya ce, kasar Masar na kokarin lalubo bakin zaren warware rikicin kasar cikin ruwan sanyi, dole ne a samu ko wace hanyar da za a bi bisa tushen girmama dokokin kasar da hukumomin kasar. Haka kuma, ya jaddada cewa, ya kamata a mayar da duk bangaren siyasa na kasar cikin shirin warware batun da sojojin kasar suka tsara .

Haka kuma, a yayin ziyarar Ashton a kasar Masar, ta gana da shugaban wucin gadi Adly Mansour da mataimakin firaminista na farko kuma ministan tsaron kasar Abdel Fattah el-Sisi da ministan harkokin waje na gwamnatin wucin gadi na kasar Nabil Fahmy da shugaban jam'iyyar SNP.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China