in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Faransa ya gana da sabon shugaban 'yan adawar Syria
2013-07-25 10:37:54 cri
Shugaban kasar Faransa Francois Hollande ya bayyana a ranar Laraba cewa, kasarsa za ta ci gaba da goyon bayan gamayyar kungiyoyin 'yan adawar Syria (CNS) don ganin an hambarar da gwamnatin da ke mulki a kasar tare da girmama tsarin demokuradiyya a kasar da fada ya wargaza.

Shugaban na Faransa ya bayyana hakan ne bayan ganawa da sabon shugaban kungiyar 'yan adawar kasar ta Syria Ahmad Jarba, inda ya ce, Faransa za ta goyi bayan gamayyar kungiyar, kuma tana shirya daukar matakan samar da tallafin jin kai da na siyasa don bai wa jama'a goyon baya.

Ya ce, kokarin da gamayyar kasashen Turai ke yi na cimma matsaya guda game da sanya wa kasar takunkumi zai hana magoya bayan shugaba Bashar al-Assad na Syria samun makamai.

A cewar hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD, yakin na Syria da aka kwashe sama da shekaru biyu ana yinsa ya halaka kimanin mutane 100,000 tare da tilasta wa mutane miliyan 1.8 kaura zuwa kasashe makwabta.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China