in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matakin soji ba zai warware rikicin Syria ba, in ji Kerry
2013-07-26 10:09:07 cri

A ranar Alhamis, sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry ya bayyana cewa daukar matakin soja ba zai warware rikicin kasar Syria ba, hanyar siyasa ce kawai mafita, don haka yake kokarin yin tattaunawa da dukkan bangarori da rikicin na Syria ya shafa, wanda zuwa yanzu yayi sanadin salwantar rayukan jama'a sama da dubu 100 a shekaru biyu da suka gabata.

Kerry ya bayyana hakan ne yayin ganawa da 'yan jarida, bayan wata ganawa da yayi da magatakardan MDD Ban Ki-Moon.

Ya ce sun dage kan kokarin hada bangarorin biyu kan tebur tattaunawa a karo na biyu a Geneva, domin a aiwatar da matakai da aka cimma a taron Geneva na farko, kuma zasu ci gaba da kokarin ganin an cimma nasara nan ba da dadewa ba.

A nasa bangare, Ban yace wajibi ne bangarorin su daina daukar duk wani mataki na soji da fadace –fadace kuma ya zama dole a yi zaman tattauanawa a Geneva game da shimfida zaman lafiya a Syria, nan ba da dadewa ba, kamar yadda Mr Kerry da Mr Lavrov suke bada shawara, inda ya kara da cewa shi da wakilin musamman na AU da MDD kan batun na Syria, Lakhdar Brahimi, za su yi kokarin tabbatar da kiran wannan zaman ganawa ba tare da bata lokaci ba. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China