in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ta samu wasika daga ma'aikatar shari'a ta kasar Amurka game da batun Snowden
2013-07-26 16:48:48 cri
A ranar 25 ga wata, wani jami'in hukumar kula da harkokin yada labaru na ma'aikatar shari'a ta kasar Rasha ya fada wa kafofin yada labaru cewa, a ranar 24 ga wata, ma'aikatar ta samu wasika daga babban joji na ma'aikatar shari'a ta kasar Amurka Eric Holder game da batun Snowden, inda ya bayyana ra'ayoyinsa game da matsayin Snowden, kuma ya bukaci Rasha da ta mika Snowden kasar Amurka ko kuma ta kore shi daga kasar.

Bisa labarin da kafofin yada labaru na kasar Rasha suka samu, an ce, a ko wace rana, Amurka ta kan tattauna batun Snowden da kasar Rasha, kuma ta ja kunnen Rasha game da babbar illa da za a kawo wa dangantakar kasashen biyu, idan har Rasha ta baiwa Snowden mafaka.

Ban da wannan kuma, jakadan Amurka da ke kasar Rasha Michael kelhol ya bayyana a shafinsa na Twitter cewa, Amurka ba za ta bukaci Rasha ta mika Snowden ba, amma ta bukaci Rasha da ta kore shi.

Yanzu, Snowden yana jiran sakamakon hukunci da Rasha ta yanke masa game da rokonsa na neman mafaka.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China