in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Togo ta kara samun cigaba a fannin kyautatuwar zaman al'umma
2011-12-21 15:11:27 cri
Kasar Togo ta kasance kasa ta biyu daga cikin kasashe takwas na kungiyar tattalin arziki da kudi ta kasashen yammacin Afrika (UEMOA) kuma kasa ta biyar daga cikin kasashe goma sha biyar na kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ta yammancin Afrika (CEDEAO) a fannin cigaban zaman al'umma, a cewar sakamakon bincike na kasa da kasa na shekarar 2011 bisa cigaban zaman al'umma da aka gabatar a ranar Talata a birnin Lome.

Wannan kundi ya rataya bisa damar dake tafiya da manufar cigaban al'umma zuwa wasu sabbin kalubale da suka shafi musammun ma matsalar banbance banbance dake kamari tsakanin al'ummomi da kuma yawan barazana da muhalli ke fuskanta.

Wakiliyar dindindin ta kungiyar PNUD dake kasar Togo, Madam Khadiata Lo N'diaye ta bayyana cewa wannan sakamakon bincike ya maida hankali ga adalci da karko bisa muhimmancin yin kira ga kasashen duniya kan manufofin siyasar da ake aiwatarwa da mulki nagari a duniya.

"hakan ya sami asali ne bisa yin la'akari da cewa samun bunkasuwa ba ya nufin jin dadin al'ummomi daga ribar da cigaba ya janyo" ta kara fadi.

Gabatar da wannan sakamakon bincike ya zo a daidai lokacin da kundin farko na dabarun kawar da talauci na (DSRP) ya zo karshensa wanda kuma tuni ake fara tattaunawa bisa manyan matakan da suka shafi kundi na biyu na shekarar 2012 zuwa ta 2013.

A halin yanzu bunkasuwar tattalin arzikin kasar Togo na kewaye da kashi 4 cikin 100, a yayin da kaso 61.7 na al'ummar kasar kusan miliyan 6 suke fama da talauci.(Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China