in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Togo ta soke ikon kariya na hukuncin shari'a na tsohon shugabanta
2013-01-18 13:29:20 cri
Bisa labarin da aka samu daga kafofin dillancin labarai na kasar Togo a ranar Alhamis 17 ga wata, an ce, ran 16 ga wata, majalisar dokokin kasar Togo ta kawar da ikon kariya na hukuncin shari'a na tsohon shugabanta Agbeyome Kodjo, don nuna wa hukumomin da suka shafi harkokin dokokin kasar goyon baya yayin da suke yin bincike kan dalilai na tashin gobara masu tsanani guda biyu da suka faru cikin watan nan da muke ciki.

Bisa labarin da aka samu, an ce, an kama Agbeyome Kodjo wanda a halin yanzu shi ne shugaba na wata jam'iyyar adawa a gidansa da ke birnin Lome, bayan awoyi da dama da aka sanar da kawar da ikon kariyar na hukuncin shari'a a kansa, daga bisani kuma 'yan dokan kasar sun yi masa tambayoyi. Kafin wannan kuma, sun kuma yi wa mataimakin shugaban jam'iyyar bincike bisa wannan dalili.

Ran 10 da 12 ga watan da muke ciki, an samu tashin gobara masu tsanani a kasar Togo har sau biyu, ko da babu wanda ya rasa ransa ko jikkata cikin gobarar, amma, hakan ya haddasa barna mai tsanani. Bayan binciken da rundunar 'yan sandan kasar suka yi, an ce, Agbeyome Kodjo na da hannu cikin wadannan hadarurruka. Shi ya sa, don gudanar da binciken da ake yi, hukumar gurfanar da mutane a kotu ta kasar ta bukaci majalisar dokokin kasar da ta kawar da ikon kariya na hukuncin shari'a na Agbeyome Kodjo.

Agbeyome Kodjo shi ke matsayin shugaban majalisar dokokin kasar Togo tsakanin shekarar 1999 da ta 2000. Ko da ya sauka daga matsayin a shekara ta 2000, yana ci gaba da samun kariyar iko na hukuncin shari'a na mambobin majalisar dokokin kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China