in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An shirya liyafar taya murnar cika shekaru 40 da kulla dangantakar diplomasiyya tsakanin kasashen Sin da Togo
2012-09-19 17:08:12 cri
A ranar 19 ga wata, a nan birnin Beijing, kwamitin kula da harkokin sada zumunta tsakanin Sin da kasashen waje, da kwamitin sada zumunta tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika sun shirya liyafar taya murnar cika shekaru 40 da kulla dangantakar diplomasiyya tsakanin kasashen Sin da Togo. Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Zhai Jun da mataimakin shugaban kwamitin sada zumunta da ke tsakanin kasar Sin da kasashen waje Feng Zuoku, da jakadan kasar Togo da ke kasar Sin Nolana Ta Ama sun halarci bikin.

A cikin jawabin fatan alheri da ya yi, Mr. Feng ya ce, a cikin shekaru 40 da suka shude, wato bayan da kasashen Sin da Togo suka kulla dangantakar diplomasiyya tsakaninsu, duk da sauyawar yanayin siyasa da ake fuskanta a duniya, dangantakar bangarorin biyu ta ci gaba da habaka lami lafiya, a karkashin goyon baya da kulawa daga shugabannin kasashen biyu, bangarorin biyu na kara yin mu'amala cikin aminci, kuma mu'amalar al'adu ta ci gaba da habaka tsakaninsu, kana an samu sakamako mai gamsarwa wajen yin hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakaninsu.

Jakadan kasar Togo da ke kasar Sin Nolana Ta Ama ya ce, Togo ta nuna goyon baya ga kasar Sin, kuma an kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a tsakaninsu ne bisa amincewar da aka samu ta fuskar siyasa cikin daidaito, da cimma moriyar juna cikin nasara a fannin tattalin arziki, da mu'amalar al'adu a tsakaninsu. Ofishin jakadancin Togo da ke kasar Sin yana fatan ci gaba da fadada dangantakar sada zumunta da ke tsakanin kasashen biyu, domin dorewar hadin gwiwa tsakaninsu a dukkan fannoni.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China