in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci a kawo karshen rikicin da ke faruwa a shiyyar Great Lakes
2013-07-26 10:19:38 cri
Wakilin kasar Sin a MDD Wang Min, ya ce kamata ya yi kasashen da ke shiyyar manyan tabkunan nan na Great Lakes, su kawo karshen tashin hankali da takaddamar da ke faruwa a shiyyar, ta yadda za a samu zaman lafiya da ci gaba mai dorewa.

Wang Min wanda shi ne mataimakin wakilin kasar Sin a MDD, ya shaidawa taron kwamitin sulhu na MDD a ranar Alhamis cewa, kasar Sin tana fatan dukkan bangarorin da abin ya shafa, za su nuna dattaku da sanin-ya-kamata, aiwatar da yarjejeniyar da suka cimma bil-hakki da gaskiya, warware bakin dayan tashin hankali da takaddamar da ke faruwa a shiyyar, kana su fara yunkurin shimfida zaman lafiya da ci gaba mai dorewa.

Ya ce, nauyin da ke gaban bangarorin a halin yanzu, shi ne gaggauta tsagaita bude wuta tare da maido da zaman lafiya a gabashin Jamhuriyar demokiradiyar Congo(DCR). Inda ya yi kira ga kungiyoyin da ke dauke da makamai da su cimma yarjejeniya da gwamnatin DRC dangane da kawo karshen tashin hankali a kasar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China