in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD, ICGLR sun sanya hannu kan yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya a yankunan Great Lakes da ke Afirka
2012-08-08 11:31:28 cri
Ofishin MDD mai kula da yankin Afirka ta tsakiya (UNOCA) da taron kolin kasa da kasa game da yankunan Great Lakes (ICGLR) sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar inganta zaman lafiya a tsakiyar Afirka da kuma yankin nan na Great Lakes.

Wata sanarwa da UNOCA ta bayar a ranar Talata yayin taron kolin shiyyar da ake gudanarwa da nufin dakatar da fadan da ke faruwa a gabashin jamhuriyar demokiradiyar Congo (DRC), ta bayyana cewa, za a mayar da hankali ne kan bangarorin zaman lafiya, tsaro, hana abkuwa da kuma daidaita rikici.

Wakilin musamman na babban sakataren MDD mai kula da yankin Afirka ta tsakiya Abou Moussa, ya ce hadin gwiwa da ICGLR ya zama wajibi, domin yin hakan na taimakawa wajen bayyana yunkurin MDD na goyon bayan shiyyar da kungiyoyin da ke yankin a kokarin da suke na tunkarar kalubalen da ke barazana ga zaman lafiyan kasa da kasa.

Babban sakataren ICGLR Daniel Alphonse Ntumba Luaba Lumu, shi ne ya sanya hannu a madadin kungiyar wadda da hallara kan kasashe 11 wadanda suka hada da Angola, Burundi, Jamhuriyar Afurka ta tsakiya, Jamhuriyar Congo, Jamhuriyar demokiradiyar Congo, Kenya, Uganda, Rwanda, Sudan, Tanzanina da kuma Zambia.

Sanarwar ta ce, hadin gwiwa tsakanin UNOCA da ICGLR zai mayar da hankali ne kan wasu batutuwa tsakanin sassan biyu, wadanda suka hada da bayar da goyon baya wajen shiga tsakani, shugabanci da manufofin tsaro, baiwa mata kwarin gwiwar shiga harkokin hana abkuwa da daidaita rikici. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China