in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a yi shawarwari a tsakanin bangarori uku a sabon zagaye kan batun Syria a ranar 25 ga wata
2013-06-22 16:33:00 cri
Mataimakin kakakin babban sakataren MDD Eduardo Del Buey ya sanar a cibiyar MDD dake birnin New York na kasar Amurka a ranar 21 ga wata cewa, za a yi shawarwari a tsakanin bangarori uku wato Rasha, Amurka da MDD a sabon zagaye kan batun Syria a birnin Geneva a ranar 25 ga wata.

A gun taron manema labaru da aka gudanar a wannan rana, Del Buey ya bayyana cewa, wakilin musamman na MDD da kungiyar tarayyar kasashen Larabawa kan batun Syria Lakhdar Brahimi zai jagoranci tawagar wakilan MDD don halartar shawarwarin.

Kana Del Buey ya nuna damuwa ga halin rayuwa da kananan yara na kasar Syria ke ciki.

A ranar 11 ga watan Janairu na bana, Brahimi ya taba yin shawarwari tare da mataimakin ministan harkokin waje na kasar Rasha Mikhail Bogdanov da mataimakin sakataren harkokin waje na kasar Amurka William Burns a birnin Geneva don tattauna shirin warware rikicin kasar Syria ta hanyar siyasa, amma bangarorin uku ba su cimma daidaito ba. A farkon watan Mayu na bana, sakataren harkokin waje na kasar Amurka John Kerry ya kai ziyara a kasar Rasha, inda shi da ministan harkokin waje na kasar Rasha Sergei Lavrov suka bada shawarar gudanar da taron kasa da kasa kan batun Syria karo na biyu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China