in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da gasar Super Cup ta kasar Italiya a birnin Rome
2013-07-05 15:56:59 cri
A ranar 27 ga wata, hukumar kawancen wasan kwallon kafa ta kasar Italiya ta sanar da cewa, za a gudanar da gasar Super Cup ta shekarar 2013 a birnin Rome, babban birnin kasar Italiya daga ranar 18 ga watan Agusta mai zuwa.

A shekarar 2009, an gudanar da gasar karo na farko a birnin Beijing dake kasar Sin, gasar da ta samu babbar nasara. Daga baya, aka sake gudanar da ita a shekarar 2011 da kuma 2012 a birnin Beijing. Bisa yarjejeniyar da aka daddale a tsakanin Sin da Italiya, za a gudanar da gasar a shekarar 2013 ko 2014 a kasar Sin. Sabo da haka, batun ko za a sake yin gasar a birnin Beijing ko a'a, ya jawo hankalin masu sha'awar wasan kwallon kafa na kasar Sin kwarai da gaske.

A ranar 27 ga wata, hukumar kawancen wasan kwallon kafa ta kasar Italiya ta tsaida kudurin gudanar da wannan gasa ta Super Cup ta bana a kasar Italiya. Zakara a gasar Serie A ta Italiya a karon da ya gabata wato kungiyar Juventus, da zakarar gasar Italian Cup kungiyar Lazio ne za su taka leda a gasar ta Super Cup a filin wasa na Olympics, dake birnin na Rome a ranar 18 ga watan na Agusta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China