in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kulaf din Gremio ya yanke hukuncin sallamar Kocinsa Vanderlei Luxemburgo
2013-07-05 15:52:32 cri
Guguwar sauyi ta yi awon gaba da kujerar tsohon kocin kulaf din Real Madrid Vanderlei Luxemburgo, a kulaf din da yakewa aiki yanzu haka, inda rahotannin baya-bayan nan suka tabbatar da cewa mahukuntan Kulaf din nasa na Gremio dake Porto Alegre, sun yanke shawarar korar kocin nasu, saboda a cewarsu daukar wannan mataki ne kawai zai ceci kulaf din daga durkushewa, duba da yadda alaka tsakanin 'yan wasa da koci Luxemburgo ta tabarbare.

Luxemburgo mai shekaru 61 da haihuwa, wanda a baya ya taba horas da 'yan wasan kasar Brazil, ya shiga tsaka mai wuya ne dai tun lokacin da kulaf dinsa ya sha kashi a hannun kulaf din Independiente Santa Fe na Colombia a gasar cin kofin Libertadores da aka buga cikin watan da ya gabata.

Da yake karin haske don gane da wannan batu a ranar Asabar din data gabata, manajan kulaf din na Gremio Rui Costa, cewa yayi lokaci yayi da za a dauki matakin daidaita al'amura a wannan kulaf, tun kafin al'amura su karasa lalacewa, ciki kuwa hadda shawarar da aka yanke ta sallamar kocin na yanzu.

Yayinda koci Luxemburgo ke sallama da kulaf din na Gremio, masu horas da 'yan wasa kamarsu Celso Roth, da Renato Gaucho, da Muricy Remalho, na cikin wadanda ake zaton za a maye gurbinsa da daya daga cikinsu. Kulaf din na Gremio dai shine na 7 a jadawalin kulaflikan dake ajin kwararrun kasar ta Brazil, inda yake da maki 8 cikin wasanni 5 da ya riga ya buga. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China