in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar wasan kwallon kafa ta nahiyar Afirka za ta tabbatar da dan wasan kwallon kafa mafi kyau na nahiyar Afirka na shekarar 2011 a wannan mako
2011-12-21 09:04:58 cri
A ran 15 ga wata, hukumar wasan kwallon kafa ta nahiyar Afirka ta gabatar da jerin sunayen 'yan wasa 5 da suka shiga takarar zama dan wasan kwallon kafa mafi kyau na nahiyar Afirka na shekarar 2011, 'yan wasan sun hada da Samuel Eto'o daga kasar Kamaru, Yaya Touré daga kasar Cote d'Ivoire, Seydou Keita daga kasar Mali, Andre Ayew daga kasar Ghana, da kuma Moussa Sow daga kasar Senegal. Hukumar hadin gwiwa ta wasan kwallon kafa ta Afirka za ta sanar da sunan dan wasan kwallon kafa mafi kyau na Afirka na shekarar 2011 da aka zaba a gun bikin hukumar da za a gudanar a wannan mako.

A farkon watan Nuwanba na bana, hukumar ta gabatar da jerin sunayen 'yan wasa 10 da suka shiga takarar lashe wannan lambar yabo. Guda biyar cikinsu sun samu damar shiga zagayen karshe na takarar. Da farko ana ganin cewa, mashahuran 'yan wasa irinsu Didier Yves Drogba da George Boateng sun fi samun damar lashe wannan lambar yabo. Amma a wasu gasannin da ya shiga Drogba bai nuna kwarewa sosai ba watakila domin shekarunsa sun karu, saboda haka, a cikin jerin sunayen 'yan wasa 5 na karshe hukumar wasan kwallon kafa ta Afirka ta zabi Yaya Touré a matsayin wakilin 'yan wasan kasar Cote d'Ivoire.

Ban da haka kuma, duk da cewa Boateng ya taka rawar gani a gasannin da aka gudanar a shekaru 2 da suka wuce, amma ya sanar da janyewa daga kungiyar kasar Ghana a kwanakin baya, wannan ya zama dalilin da ya sa sunansa bai fito ba a jerin sunayen. Don haka, a jerin sunayen, ana ganin Eto'o da Yaya Toure sun fi samun damar lashe wannan lambar yabo.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China