in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Mali ta ba da lambar yabo ga dukkan ma'aikatan rukunin ba da jinya na kasar Sin
2013-07-05 12:26:58 cri
Ran 4 ga wata, a madadin shugaban kasar Mali Dioncounda Traore, ministan kula da harkokin kiwon lafiyar kasar Soumana Makadji ya ba da lambar yabo ga dukkan ma'aikatan rukunin ba da jinya na 22 da kasar Sin ta aika zuwa kasar Mali, bayan kammala ayyukansu a kasar cikin nasara, kuma yanzu haka ma'aikatan rukunin suke shirin dawowa kasar Sin.

Mr. Makadji ya nuna yabo sosai ga ayyuka da kuma halayen ma'aikatan rukunin ba da jinya na kasar Sin, inda ya yi godiya gare su domin gudumawar da suka bayar kan inganta harkokin hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya da kuma zumuncin da ke tsakanin kasashen biyu.

Bisa labarin da aka samu, ana da ma'aikata sama da 30 cikin rukunin, wadanda suka isa kasar Mali a watan Agusta na shekarar 2011, kuma yayin da suke gudanar da ayyukansu a kasar Mali, sun ba da gudumawa sosai a fannin kiwon lafiya na kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China