in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sinawa dake kasashen waje sun nuna goyon baya ga gwamnatin kasar Sin da ta dauka matakan yaki da ta'addanci
2013-07-01 20:48:57 cri
A kwanakin baya, Sinawa dake kasashen waje sun yi Allah wadai da harin da aka kai a jihar Xinjiang dake kasar Sin, kana sun bayyana cewa, suna nuna goyon baya ga gwamnatin kasar Sin da ta dauka matakan yaki da ta'addanci bisa dokoki, kiyaye zaman lafiya a jihar Xinjiang da kuma tabbatar da tsaron jama'a da dukiyarsu.

Shugaban kungiyar sada zumunta a tsakanin Amurka da Sin Qiao Fengxiang ya yi tsammani cewa, harin da aka kai a jihar Xinjiang a kwanakin baya ba matsalar kabila ko addini ba ce, yaki ne dake tsakanin 'yan aware da masu yaki da 'yan aware, da kuma tsakanin masu tada zaune tsaye da masu tabbatar da dinkuwar kasar Sin. Hare-haren ta'addanci sun haddasa mutuwa da raunatar jama'a tare da hasarar dukiya. Sinawa dake kasashen waje sun nuna goyon baya ga gwamnatin kasar Sin da ta tabbatar da zaman lafiya, daukar matakai masu dacewa, yaki da dukkan ayyukan ta'addanci, da kuma kiyaye zaman lafiya da tabbatar da tsaron jama'a da dukiyarsu a jihar Xinjiang.

Mataimakin shugaban kungiyar sa kaimi ga samun zaman lafiya da dinkuwar kasar Sin dake kasar Rasha Yuan Yi ya bayyana cewa, Sinawa dake kasar Rasha sun yi fushi sosai ga hare-hare da ayyukan kawo illa ga hadin kai da zaman lafiya a jihar Xinjiang da 'yan ta'addanci suka yi. Sinawa dake kasashen waje ciki har da Sinawa dake kasar Rasha suna nuna goyon baya ga tabbatar da dinkuwar dukkan kasar Sin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China