in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 33 sun mutu a wani fadan kabilanci a Nigeriya
2013-06-28 20:20:43 cri
A ranar Jumma'an nan 28 ga wata mazauna da kuma hukumomi a garin Jos dake jihar Filato a tsakiyar arewacin kasar Nigeriya suka tabbatar da cewa, a kalla mutane 33 ne suka mutu sakamakon wani harin da wadansu da ba'a san ko su wane ne ba suka kai masu.

Mark Lipdo, jami'in Stefanus Foundation, wata kungiya mai zaman kanta ya sheda ma kamfanin dillanci labarai na kasar Sin Xinhua cewa, mutane 33 ne aka kashe a sanyin safiyar ranar Alhamis a karamar hukumar Langtang dake jihar.

Shi ma shugaban rikon kwarya na karamar hukumar ta Langtang Narman Darko ya tabbatar da mutuwar wadannan mutane a kauyuka uku, abin da yake danganta shi da cewa, 'yan kungiyar ta'adda na Fulani ne suka aikata shi.

Kwamandan rundunar tsaro ta hadin gwiwwa a jihar Brigadier Janar Harry Ayoola shi ma ya tabbatar da mutuwar mutane da dama, amma ya ce, ba'a gama samun cikakken adadinsu ba sai dai jami'an tsaro tuni suka isa wurin, duk da suma sai da suka yi arangama da maharan kafin su samu nasarar wanzar da doka da oda, kuma ya zuwa yanzu sun kama wadansu da ake zargi da wannan hari da dama.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China