in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta tura sojoji zuwa kasar Mali don kiyaye zaman lafiya
2013-06-27 20:14:17 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Madam Hua Chunyin, ta sanar a Alhamis 27 ga wata a nan birnin Beijing cewa, bisa bukatar MDD, gwamnatin kasar Sin ta yanke shawarar tura wasu sojojin a bangaren aikin injiniya, likitoci, da dakarun kare lafiya ga rundunar kiyaye zaman lafiya ta MDD dake kasar Mali. Wannan batu zai kasance karo na farko da kasar Sin ta tura jami'an tsaro maimakon masu aikin injiniya ko likitanci zuwa kasashen waje don gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya.

A cewar Madam Hua, kasar Sin a matsayinta na daya daga cikin kasashen dake da zaunannun kujeru a kwamitin sulhu na MDD, ta dade tana ma ayyukan kiyaye zaman lafiya goyon baya, har ma ta kasance daya daga cikin kasashen da suka tura sojoji mafi yawa domin aikin.

Ya zuwa yanzu, kasar Sin ta riga ta tura jami'ai da 'yan sanda fiye da dubu 20 zuwa waje domin gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya. A halin da ake ciki kuma, akwai jami'ai da 'yan sandan kasar Sin 1645 dake gudanar da ayyukansu a wasu yankuna guda 9 dake kasashe daban daban. Haka zalika, a cikin sahun kasashe masu tasowa, kasar Sin ita ce ta fi samar da kudi ga MDD don tallafawa aikin wanzar da zaman lafiya.

Madam Hua ta kara da cewa, kasar Sin za ta ci gaba da kokarin shiga ayyukan kiyaye zaman lafiya da MDD ta jagoranta, don samar da gudummawa ga kokarin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duk duniya.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China