in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar kiyaye zaman lafiya da Sin ta tura kasar Sudan ta kudu ta dawo gida
2012-11-14 10:19:30 cri
A yammacin ranar 13 ga wata, rundunar kiyaye zaman lafiya karo na farko da Sin ta tura kasar Sudan ta kudu, ta dawo nan kasar Sin bayan da ta kammala wa'adin aikin ta na tsawon shekara daya.

Bisa bukatar MDD, a ranar 11 ga watan Nuwambar shekarar 2011, ma'aikatar ba da tsaro ga jama'a ta kasar Sin, ta tura wata rundunar kiyaye zaman lafiya ta farko yankin da MDD ke ba da kulawa a kasar Sudan ta kudu. Wannan runduna ta kunshi 'yan sanda 14. Bayan sun isa yankin, sun fuskanci kalubaloli da dama, amma duk da hakan sun taimakawa kasar wajen tabbatar da halin da ake ciki na wucin gadi, sun kuma ba da taimako ga 'yan sanda wuri tabbatar da bin doka da oda, da kuma yin kwaskwarima da sake kafa hukumar gudanar da doka da shari'a. Rundunar dai ta kammala aikinta yadda ya kamata, al'amarin da ya kafa siffar 'yan sandan kasar Sin a duniya.

An ce, a ran 12 ga watan Satumba na shekarar bana, yayin bikin bada lambobin yabo da tawagar musamman ta MDD dake Sudan ta kudu ta yi a Jubba, hedkwatar kasar, an baiwa rundunar kasar Sin lambar yabo ta "Samar da zaman lafiya", ta MDD. (Amina)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China