in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a yi taron dandalin tattaunawar batun kiwon lafiya na kasar Sin a watan Agusta
2013-05-07 20:16:48 cri
Za a yi taron dandalin tattaunawar batun kiwon lafiya na kasar Sin a tsakanin ran 16 zuwa 18 ga watan Agusta na shekarar 2013. Babban jigon wannan taro shi ne "kara hadin gwiwar harkokin kiwon lafiya tsakanin Sin da Afirka a kokarin samun sabon ci gaba a nan gaba".

Bisa labarin da wakiliyar gidan rediyo kasar Sin ta aiko mana, an ce, za a gayyaci manyan jami'an kiwon lafiya na kasashen Afirka 51 da jakadunsu da ke nan kasar Sin, jami'an kungiyoyin kasa da kasa, ciki har da kungiyar kiwon lafiya ta kasa da kasa da bankin duniya da su halarci taron, ta yadda za su iya amfana da fasahohin da kasar Sin ta samu wajen tallafawa kasashen Afirka a fannin kiwon lafiya, kuma za su tattauna kan yadda za a kara yin hadin gwiwa kan harkokin kiwon lafiya tsakanin Sin da kasashen Afirka a cikin sabon yanayin da ake ciki yanzu.

Shekarar da muke ciki shekara ce ta cika shekaru 50 da kasar Sin ta tura rukunonin likitoci zuwa kasashen Afirka. Sabo da haka, a yayin wannan taron, za a kara tattaunawa kan yadda za a yi hadin gwiwa wajen tsara manufofin kiwon lafiya kan harkokin horar da kwararru, yada fasahohin kiwon lafiya da magance karuwar masu kamuwa da cututtukan yau da kullum a kasashen Afirka. Kana kuma, za a tattauna kan yadda kasashen Sin da Afirka za su yi koyi da kuma amfani da fasahohin zamani na kiwon lafiya daga kasashe masu wadata domin ciyar da harkokin kiwon lafiya a kasashen Afirka gaba. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China