in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Akwai sojojin Faransa 3200 a kasar Mali
2013-06-27 10:35:13 cri
A ranar 26 ga wata a gun taron manema labaru da aka gudanar a birnin Paris dake kasar Faransa, ministan tsaron kasar Jean-Yves Le Drian ya bayyana cewa, a halin yanzu, yawan sojojin kasar dake kasar Mali ya kai 3200.

Le Drian ya ce, yawan sojojin kasar Faransa dake Mali zai ragu, zuwa kimanin 2000 a karshen watan Agusta, wato bayan an gama zaben shugaban kasar Mali wanda za'a yi a watan Yuli na bana. Ya zuwa karshen bana kuma, yawan sojojin Faransa dake Mali zai ragu zuwa kimanin 1000.

Le Drian ya kara da cewa, sojojin kasar Faransa kuwa yawancinsu suna hake a kewayen birnin Gao, babban birni na farko dake arewacin kasar Mali da kuma yankin Ifo Las, faffadan tsaunin dake arewa maso gabashin kasar Mali, wadanda suka taba yin yake-yake tare da kungiyoyin masu tsananin kishin addini da ta'addanci a yankin Ifo Las.

Yawan nauyin albarushin da sojojin Faransa suka kwace a maboyan masu tsattsauran ra'ayi ya kai ton 300,yayin da suke yin aikin soja a kasar Mali. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China