in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 37 suka rasu a sanadiyyar rubzawar mahakar zinari a jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
2013-06-25 11:28:09 cri
Ran 24 ga wata, shugaban wucin gadin kasar jamhuriyar Afirka ta Tsakiya Mr. Michel Djotodia ya sanar da zaman makoki na kwanaki uku a kasarsa, domin nuna juyayi ga rasuwar wasu mutane 37, a sanadiyyar rubzawar mahakar zinari da ta faru a yankin tsakiyar kasar ran 23 ga wata.

Bisa labarin da aka samu, an ce, lamarin ya faru ne a yankin mahakar ma'adinai ta Bambari, mai nisan kilomita 440 daga Banji, babban birnin kasar. Ya zuwa yanzu, an riga an tabbatar da mutuwar mutane 37, dukkansu 'yan asalin kasar, yayin da mutane da dama suka samu raunuka, kuma ake tsoron samun karin wadanda ka iya rasuwa cikin majiyyatan.

Kasar jamhuriyar Afirka ta Tsakiya dai na da wadatar ma'adinai, amma yanzu, ana gudanar da ayyukan hakar lu'u-lu'u da zinari ne ba tare da amfani da na'urori na zamani ba. Bugu da kari, cikin jimillar al'ummar kasar miliyan 4.4, yawan wadanda suke wannan aiki na hakar ma'adanai bai wuce kaso 15 bisa dari ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China