in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mohamed EL-Baradei ya bukaci shugaban kasar Masar da ya yi murabus
2013-06-23 16:44:51 cri
A ranar Asabar 22 ga watan nan da muke ciki ne shugaban jam'iyyar adawar ta National Salvation Front dake kasar Masar, kana tsohon shugaba hukumar makamashin nukiliya ta duniya, Mohamed El-Baradei ya bukaci shugaban kasar Masar Mohamed Morsi da ya yi murabus daga mukaminsa, yana mai nanata cewa, zai goyi bayan zanga-zangar adawa da gwamnatin kasar da za a yi a ranar 30 ga wata, bisa jagorancin kungiyar fafitika ta "Tamarod".

A wannan rana, jam'iyyar ta NSF ta kira taron shugabannin jihohi a birnin Alkahira. Kafin taron, mista El-Baradei ya bayyana wa kafofin yada labaru cewa, kamata ya yi Mohamed Morsi ya amsa kiran jama'a, wato yayi murabus daga mukaminsa, saboda mafi yawan jama'ar kasar Masar sun nuna rashin gamsuwa ga salon jagorancinsa.

Ban da haka, mista El-Baradei ya furta cewa, a sakamakon rashin manufofi masu kyau da Masar ke fuskanta karkashin jagorancin gwamnatin mai ci a yanzu, kasar na gamuwa da matsalolin tsanantar yanayin tattalin arziki, da rashin zaman lafiya da kwanciyar hankali, a sabili da haka, ana sanya ran samun canji. El-Baradei ya yabi kungiyar ta Tamarod, yana mai cewa, al'ummar Masar na share fage ga gwagwarmayar da za a shiga a ran 30 ga wata.

Kafin wannan, kungiyar fafitika ta Tamarod ta yi kira ga jama'ar kasar da su yi babbar zanga-zanga a ranar 30 ga wata, wato ranar cika shekara guda da kama aikin shugaba Morsi a matsayin sabon shugaban kasar, matakin da 'yan adawar ke fatan zai gaggauto da gudanar babban zaben kasar.

Domin mai da martani ga wannan mataki na 'yan adawa, bangare magoya bayan shugaba Morsi, sun riga sun yi zanga-zangar nuna gamsuwa da salon jagorancinsa a ranar 21 ga wata. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China