in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahukuntan Sham sun yi Allah wadai da katse dangantakar diplomasiyya da Masar ta ce ta yi da gwamnatin al-Assad
2013-06-16 20:55:33 cri
Mahukuntan kasar Sham sun bayyana matakin da kasar Masar ta dauka na katse dangantakar diplomasiyya da gwamnatin shugaba Bashar al-Assad, a matsayin wani mataki wanda sam bai dace ba.

Bugu da kari, gwamnatin kasar ta Sham ta ce, wannan matakin da shugaba Morsi ya dauka ba wani abu ba ne, illa aiwatar da manufofin kungiyar nan ta 'yan uwa musulmi ko "Muslim Brotherhood" a turance.

Da yake tsokaci kan wannan batu, ministan watsa labarun kasar Sham Omran al-Zoubi cewa ya yi, tuni ya dace shugaba Morsi ya dauki makamancin wannan mataki na yanke huldar diplomasiyya da kasar Isra'ila, wadda a cewarsa ke ci gaba da kisan Palasdinawa.

Wannan dai mataki da mahukuntan kasar ta Masar suka dauka, tare da ragowar masu adawa da gwamnatin kasar ta Sham, na zuwa ne daidai lokacin da rundunar sojin kasar ta Sham ke samun gagarumin rinjaye kan 'yan adawa a sassan kasar daban daban.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China