in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD na sa ran ganawa da sabbin shugabannin kasar Sin
2013-06-16 17:10:53 cri
Kwanan baya, Ban Ki-moon, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya ce, yana sa ran ganawa da sabbin shugabannin kasar Sin, ya kuma yi fatan cewa, MDD za ta inganta kyakkyawar huldar abokantaka a tsakaninta da kasar Sin.

Bisa gayyatar da gwamnatin kasar Sin ta yi masa, mista Ban zai kawo wa kasar Sin ziyarar aiki daga ranar 18 zuwa 21 ga wata. A lokacin da yake zantawa da manema labaru kafin ya tashi zuwa kasar Sin, mista Ban ya bayyana cewa, akwai huldar abokantaka mai danko a tsakanin kasar Sin da MDD. Ya ce, kasar Sin na daya daga cikin muhimman kasashe mambobin MDD. Kuma sakamakon bunkasuwar tattalin arzikinta ya sa kasar Sin kara yin tasiri a duk fadin duniya. Mista Ban yana fatan kasar Sin za ta kara ba da gudummawa a duniya wajen kiyaye zaman lafiya da kara azama kan samun ci gaba mai dorewa.

Har wa yau kuma, mista Ban ya ce, a lokacin ziyararsa a kasar Sin, zai yi shawarwari da shugabannin kasar dangane da wasu muhimman al'amuran kasa da kasa da na shiyya-shiyya. Kana kuma zai yi musayar ra'ayoyi da shugabannin kasar Sin game da batun samun dawamammen ci gaba.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China