in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira ga Sudan da Sudan ta Kudu da su yi hakuri da juna
2013-06-13 20:42:16 cri
Kwanan baya, kasar Sudan ta hana kasar Sudan ta Kudu ta yi amfani da bututun man fetur da ke kasar domin sayar da man fetur zuwa ketare. Dangane da lamarin, Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana a ran 13 ga wata a nan Beijing cewa, tabbatar da samar da man fetur da kuma sayar da shi zuwa ketare yadda ya kamata daga Sudan ta Kudu ta shafi babbar moriyar kasashen 2 ta fuskar tattalin arziki, haka kuma zai yi tasiri kan huldar da ke tsakaninsu duka.

A don haka kasar Sin take kira ga kasashen 2 da su kasance cikin nitsuwa da yin hakuri, su nuna wa juna kulawa kan muhimman batutuwan da suka mai da hankali a kai. Ya kamata su aiwatar da yarjejeniyoyin da suka cimma a baya, a kokarin kau da sabanin da ke tsakaninsu yadda ya kamata da kuma kiyaye huldar da ke tsakaninsu ta hanyar yin tattaunawa da shawarwari na cude-ni-in-cude-ka.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China