in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi kira ga kasar Ghana da ta tabbatar da tsaron 'yan kasar
2013-06-09 11:00:56 cri
A ranar 8 ga wata, yayin da kakakin ma'aikatar kula da harkokin kasuwanci ta kasar Sin Shen Danyang ke zantawa da manema labaru game da tsare wasu Sinawa da ake tuhume su da haka zinariya ba bisa ka'ida ba, ya bayyana cewa, yana fatan kasar Ghana za ta yi la'akari bisa ga hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakaninsu, don daidaita batun yadda ya kamata, ta yadda za a tabbatar da tsaron Sinawa da dukiyoyinsu a Ghana.

Shen Danyang ya jaddada cewa, ma'aikatar kula da harkokin kasuwanci ta Sin ta dora muhimmanci sosai game da wannan batu, kuma ta yi hadin gwiwa da ma'aikatar kula da harkokin wajen kasar Sin da ofishin jakadancin Sin da ke kasar Ghana don yin tuntubawa da shawarwari cikin aminci tare da kasar Ghana. Shen Danyang ya ja kunne sauran Sinawa dake aiki a kasashen waje, su bi hanyar ya kamata wajen yin aiki a kasashen waje, da shiga cikin kasar, da yin aiki da samun iznin zama bisa ka'ida, don magance ayyukan da za su lahanta hakkin Sinawa da tsaronsu.

Kwanan baya ne dai, hukumomin shari'a na kasar Ghana sun cafke Sinawa sama da 100 da aka tuhume su da haka zinariya ba bisa ka'ida ba.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China