in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Ghana ya gana da tawagar jam'iyyar JKS
2013-05-18 16:37:55 cri
A Jumma'a 17 ga wata, mataimakin shugaban kasar Ghana, Kwesi Bekoe Amissah-Arthur, ya gana da tawagar jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin wadda Huang Xianyao, babban jami'in hukumar lardin Guangdong dake kudancin kasar Sin, ya jagoranta, a fadar shugaban kasar Ghana.

A lokacin ganawar, Mista Amissah-Arthur ya ce Ghana na son yin amfani da tallafin da kasar Sin ke ba ta, don samun wani ci gaban tattalin arziki wanda saurinsa zai kai na kasar Sin. Haka zalika, a cewar Mista Amissah-Arthur gwamnatin kasar Ghana za ta ci gaba da tsayawa kan manufar kasar Sin daya tak a duniya.

A nasa bangaren, Mista Huang Xianyao ya ce, jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana dora muhimmanci sosai kan dangantakar dake tsakaninta da jam'iyyar NDC ta Ghana, don haka tana fatan kara hadin gwiwa tsakanin jam'iyyun 2, da ci gaba da kokarin kyautata huldar dake tsakanin kasashen 2.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China