in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta riga ta dauki matakan kiyaye halaltattun hakkokin Sinawan da aka tsare su a Ghana
2013-06-06 16:57:14 cri
Ranar 6 ga wata, a nan Beijing, Hong Lei, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya fayyace cewa, kasar Sin ta riga ta tuntubi kasar Ghana, inda ta bukace ta da ta dauki hakikanin matakan tabbatar da tsaron lafiya da halaltattun hakkokin Sinawan da aka tsare su a Ghana.

Hong Lei ya kara da cewa, ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sake tunatar da Sinawan da ke kasar Ghana da su bi dokokin wurin a tsanake, kada su saba wa dokokin kasar. Kuma ma'aikatar da ofishin jakadancin kasar Sin da ke Ghana za su ci gaba da ba da kariya da taimako ga Sinawan da ke kasar, a kokarin tabbatar da tsaron lafiyarsu da halaltattun hakkokinsu.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China