in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a kafa wata gidauniyar da za ta taimakawa kasashen yankin Sahel fuskantar matsalar karancin abinci
2012-04-28 16:53:53 cri
Babban darektan hukumar kula da abinci da noma ta Majalisar Dinkin Duniya wato FAO mista Jose Graziano Da Silva ya sanar a Brazaville a ranar Jumma'a 27 ga wata da kafa nan da dan lokaci kalilan wata gidauniyar da za ta taimakawa kasashen yankin Sahel fuskantar matsalar karancin abinci.

Gidauniyar za ta rika samun kudaden da za ta gudanar da aikinta daga kasashen dake fitar da man fetur.

"Mun sanya kira domin ganin an tabbatar da kafa wannan asusun da zai samu kudi daga kasashen dake fitar da man fetur da ma'adinai, ta yadda za mu samu damar tinkarar matsalar karancin abinci a yankin Sahel da kuma cikin kusurwar Afrika." in ji mista Jose Graziano Da Silva a yayin wani zaman taron shiyya na hukumar FAO kan nahiyar Afrika karo na 27 da aka gudanar a birnin Brazaville. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China