in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da shirin tallafi ga tattara arzikin cikin gida a kasar Nijar
2013-04-05 15:26:15 cri
Ministan fasali da cigaban karkara na kasar Nijar Amadou Boubacar Cisse ya kaddamar da shirin tallafi ga tattara arzikin cikin gida da kyauttata harkokin tattalin arziki da kudi (PAMOGEF).

A cikin jawabinsa, ministan kasar ya nuna yabo kan dangantakar dake tsakanin kasar Nijar da bankin BAD, kafin ya bayyana gamsuwarsa bisa kafa wannan shiri da zai kara kyautata kwarewar kasar Nijar ta fuskar cigaban tattalin arziki da zaman al'umma a kasar Nijar.

Kuma wannan a cewar minista Cisse shi ne na kara gyara yanayin harkoki, baiwa 'yan damar cin gajiyar arzikin ma'adinai da kuma shigar da bangarori daban daban wajen kula da harkokin cigaban kasa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China