in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mu'amalar da ake yi tsakanin jam'iyyun kasashen Nijer da Sin za ta raya huldar kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi
2013-04-12 17:01:22 cri
A ranar 11 ga wata, yayin da mataimakin sakatare janar na jam'iyyar PNDS-Tarayya wato jam'iyyar da ke mulki a jamhuriyar Nijer Issoufou katambé ke zantawa da wakilinmu a nan birnin Beijing, ya bayyana cewa, bayan da aka zurfafa mu'amala da ke tsakanin jam'iyyun kasashen Nijer da Sin, kuma za a kara yin mu'amala da hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Katambe ya kara bayyana cewa, a cikin 'yan shekarun nan, mu'amala da ke tsakanin jam'iyyun kasashen biyu ta kara samun ingantuwa. A wannan karo ne, jam'iyyar da ke mulki a jamhuriyar Nijer ta tura wata tawagar da ke kunshe da mutane 15 da suka fito daga jihohi 8 na kasar, don su samu yin nazari a kasar Sin. Ta hanyar yin nazari kuwa, kasar Nijer tana fatan za ta kara zurfafa hadin gwiwa tsakaninta da kasar Sin a fannoni aikin noma, ilmi, da kiwon dabbobi, da makamashi, da shimfida hanyoyi da sauransu, don taimakawa aikin raya tattalin arziki a kasar.

Kwanan baya, bisa goron gayyata da sashen kula da harkokin tuntubawar jam'iyyun kasashen duniya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ya yi, tawagar yin nazari ta jam'iyyar PNDS-tarayya ta jamhuriyar Nijer ta kawo ziyara a nan kasar Sin. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China