in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yan adawar Syria sun amince bisa manufa su halarci tattaunawar Geneva
2013-05-27 10:43:20 cri

Yan adawar Syria sun bayyana a ranar Lahadi cewa, sun amince bisa manufa su halarci tattaunawar zaman lafiyar da za a yi a birnin Geveva.

Babban jami'in kungiyar galibinsu mazauna ketare(SNC) Louay Safi ya shaidawa manema labarai a Istanbul na kasar Turkiya cewa, shugaba Bashar al-Assad ba zai kasance a cikin maganar makomar Syria ba.

Ya kuma ce, suna maraba da shirin kasa da kasa na samar da zaman lafiya a kasar, kuma duk wani kokari na samun nasarar shirin wajibi ne ba za a sanya shugaba mai ci a ciki ba.

Tun a ranar Alhamis ne babbar kungiyar adawa ta Syria, ta gudanar da tattaunawa a Istanbul don bayyana matsayinta game da taron wanzar da zaman lafiya karo na biyu game da Syria da za a yi a Geneva

Bugu da kari, yayin taron na Istanbul, ana sa ran kungiyar ta SNC ta zabi sabon shugabanta wanda zai maye gurbin Moaz al-Khatib wanda ya sauka daga mukaminsa a watan Fabrairu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China