in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi maraba da kokarin kasar Sin na taimakawa don ganin an kau da makaman nukiliya a zirin koriya
2013-05-25 16:16:38 cri
Babban magatakardan MDD Ban Ki-Moon a jiya juma'a 24 ga wata ya bayyana matukar yabawar sa ga kasar Sin bisa ga kokarin ta na ganin an kau da makaman nukiliya a zirin Koriya, yana mai cewa ganawar da Shugaban kasar Xi Jinping yayi da Choe Ryon Hae manzo na musamman na Shugaban kasar jamhuriyar demokradiya na kasar Koriya DPRK Kim Jong Un a birnin Beijing ya haifar da wani tabbaci a wannan hanyar.

A cikin wata sanarwa da kakakinsa ya bayar a birnin Entebbe na kasar Uganda inda babban magatakardar yanzu haka yake ziyarar aiki,yace zai ci gaba da bin sahun wannan tattaunawa kuma a shirye yake yayi duk abinda ya kamata don ganin wannan kokarin da kasar Sin ke son yi ya samu karbuwa.

A lokacin ganawar a nan Beijing Shugaba Xi ya jaddada matsayin da Sin ta dauka na ganin an kau da makaman nukiliya a zirin Koriya, yana mai cewa ya kamata wannan aniya dukkannin bangarorin da abin ya shafa su tabbatar da ganin ta samu karbuwa a ko wane irin yanayi kuwa hakan zai kawo.

Kau da makaman nikiliya da zaman lafiya da kwanciyar hankali a zirin Koriya wani buri ne da al'ummomin wurin ke son ganin ya tabbata a yankin, inji Mr Xi.

A nashi bangaren manzo na musamman Choe Ryong Hae wanda ya isar da wasikar Shugaba Kim Jong Un a lokacin ganawar sa da Shugaba Xi,ya ce wannan burine na hakika da kasar Jamhuriyar demokradiya na koriya ke fatan ganin an cimma domin samar da zaman lafiya a yankin, a samu inganta tattalin arziki da kuma rayuwar al'umma.

A cewar shi Kasar DPRK a shirye take ta yi aiki da bangarorin da abin ya shafa domin warware dukkan matsalolin da ya shafi hakan ta hanyar tattaunawa da tuntubar juna da suka hada da tattaunawa da kasashe shida, sannan kuma kasar sa tana da aniyar rungumar duk wani shawara da aka bayar da zai kiyaye zaman lafiya da karko a zirin koriya. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China