in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Rasha suna fatan za a warware batun nukiliya na yankin Koriya ta hanyar diplomasiyya
2013-04-13 16:47:04 cri
A kwanakin baya, halin yankin Koriya ya jawo hankalin kasa da kasa sosai. A ranar 12 ga wata, ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta bayyana cewa, kasar Sin tana son yin kokari wajen sassauci kan batun yankin Koriya ta hanyar yin shawarwari, da sa kaimi wajen warware matsaloli ta hanyar yin shawarwari, ciki har da sake bude shawarwari a tsakanin bangarori shida.

A wannan rana kuma, mataimakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Rasha Igor Morgulov ya bayyana yayin da yake ganawa da jakadan kasar Koriya ta arewa dake kasar Rasha cewa, kasar Rasha ta yi kira ga kasar Koriya ta arewa da ta kwantar da hankali, kuma kada ta dauki matakan tsananta halin da ake ciki a yankin Koriya. Kafin wannan, shugaban kasar Rasha Vładimir Putin ya taba bayyana cewa, bai kamata bangarori daban daban da abin ya shafa su dinga tsananta halin yankin Koriya ba, ya kamata su warware matsaloli ta hanyar yin shawarwari cikin lumana.

Sakataren harkokin waje na kasar Amurka John Forbes Kerry ya bayyana yayin da yake ziyara a kasar Koriya ta kudu a ranar 12 ga wata cewa, kasar Amurka tana son yin shawarwari tare da kasar Koriya ta arewa ta hanyar yin shawarwari a tsakanin bangarori shida ko kuma shawarwari a tsakanin bangarorin biyu, amma ya kamata kasar Koriya ta arewa ta bi ka'idojin kasa da kasa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China