in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Koriya ta arewa ta ce makamai masu linzamin da ta harba wani bangare ne na atisayen soja da nufin kare kai
2013-05-20 20:14:15 cri
Kamfanin dillancinlabarai na kasar koriya ta arewa (KCNA) ya ruwaito kasar Koriya ta arewa na fada a ranar Litinin cewa, kasar ta harba makamai masu linzami ne a matsayin wani bangare na atisayen soja domin ta kare kanta.

Kwamitin samar da zaman lafiya na Koriya ta arewa ya fada cikin wata sanarwa cewa, kasar tana da 'yancin gudanar da atisayen da kasashen Amurka da Koriya ta kudu suka yi Allah-wadai da shi.

Wannan shi ne karo na farko da Pyongyang ta mayar da martani ga harba makamai masu linzamin da ake zarginta da aikatawa, inda ta zargi Washington da Seoul da gudanar da atisayen soja cikin hadin gwiwa da na'urorin harba bama-bamai.

Ofishin shugaban kasar Koriya ta kudu ya bukaci Koriya ta arewa da ta dakatar da tsananta halin da ake ciki a zirin Koriya, bayan da Pyongyang ta harba makamai masu linzami masu cikin gajeren zango a yankin ruwanta a ranar Asabar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China