in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Koriya ta arewa ta rufe yankin masana'antu na Kaesong
2013-04-09 20:55:08 cri
Game da lamarin rufe yankin masana'antu na Kaesong da kasar Koriya ta arewa ta sanar, Mr. Hong Lei, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana a nan birnin Beijing, cewar kasar Sin na fatan bangarorin da abin ya shafa su yi abubuwan da za su taimakawa kokarin tabbatar da kwanciyar hankali a yankin Koriya.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, a ran 8 ga wata, kasar Koriya ta arewa ta sanar da rufe yankin masana'antu na Kaesong, sannan a yau 9 ga wata, ta ba da shawara ga hukumomi da masana'antu na kasashen waje da baki masu yawon bude ido a kasar da su tsara shirin janye jiki daga kasar. Game da wannan lamari, Hong Lei ya ce, bangaren Sin na adawa da dukkan matakan da za su tsananta halin da ake ciki, kuma ya nuna ki amincewa da dukkan matakan da za su kawo illa ga halin kwanciyar hankali da ake ciki a yankin Koriya.

Sannan, ya sake yin kira ga bangarorin da abin ya shafa da su yi kokari wajen tabbatar da zaman lafiya da fitar da yanki daga mawuyacin hali. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China